Добавить новость
smi24.net
World News in Dutch
Ноябрь
2016

Abubuwa 5 da Obasanjo ya fada game da gwamnatin su Buhari

0

– Tsohon shugaban kasa Cif Olusegun Obasanjo ya zargi wasu tsare-tsaren kasar nan

– Wannan karo Cif Obasanjo ya zo wa shugaban kasa Muhammadu Buhari da zafi

– Haka nan tsohon shugaban kasar yayi kaca-kaca da tsohin shugaban kasa Dakta Goodluck Jonathan

 

 

 

 

 

Tsohon shugaban kasar nan, Cif Olusegun Obasanjo ya gabatar da wata kasida jiya, a Legas, inda yayi kaca-kaca da wasu tsare-tsare na Kasar nan. Jaridar Premium Times ce dai ta rahoto wannan labari. Mu kuma mun kawo maku muhimman abubuwa daga cikin abin da ya fada:

KU KARANTA: Shugaba Buhari yayi raddi ga Buba Galadima

  1. Babban ciwon kan kasar nan itace Majalisa. Ko da an gyara Bangaren shari’a, ya za ayi da ‘Yan Majalisa, wanda sun fi kowa rubuewa?
  2. Duk duniya babu inda ake da ‘yan majalisa irin na Najeriya. Albashin kowane Sanata ko dan majalisar Tarayya ya haura Miliyan goma a kowane wata. Dole a hukunta wadanda suka yi badakalar kasafin kudi.
  3. Rashawa ta shiga har gidan Soji, Sojojin Kasar sun koma sata cikin ‘yan shekarun bayan nan. Ta yaya Janar na Soja zai saci kudin sayen makamai.
  4. Bai dace Shugaba Buhari ya karbo bashin Biliyan $30 ba
  5. Gwamnati ta rika jawabi a kai-a kai ga ‘Yan Kasa a irin su Rediyo da Talabijin

A biyo mu a shafin mu na Tuwita @naijcomhausa    

 

The post Abubuwa 5 da Obasanjo ya fada game da gwamnatin su Buhari appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Read Nigerian newspapers 24/7.















Музыкальные новости






















СМИ24.net — правдивые новости, непрерывно 24/7 на русском языке с ежеминутным обновлением *