Добавить новость
smi24.net
World News in Dutch
Июнь
2016

An kona wani mutum kurmus a Jihar Delta

0

-Hotuna sun fara yaduwa na hukuncin da wasu mutane suka yankema wani mutum

-Mutumin yayi ma wata yarinya fyade ne na fitan hankali

-Mutanen cikin fushi,suka banka masa wuta har lahira

Wani abun takaici ya faru a Unguwar Ekuigbo dake karamar hukumar Ughelli ta Arewa a Jihar Delta a ranar laraba 29 ga watan yuni, yayinda yan unguwa suka banka wa mutum wuta, sai dai ya tashi a lahira.

inda aka banka ma wani wuta

Abun zargin na cikin yan daban da yi ma wata yarinya yar kasuwakuma yar shekara 22 mai sayar da abincin kifi fyade ,a ranar litinin 27 ga watan yuni.

Jaridar daily post ta bada rahoton cewa  kakakin hafsan yan sanda,Mr. Celestine Kalu, ya tabbatar da labarin, yace an fara gudanar da bincike akan al’amarin. Mr. Celestine yace budurwar na jinya a asibitin central da ke Jihar.

Daga baya munyi iyakan kokarin sake ganawa da kakakin yan sanda domin samun cikon labarin  amma bamu samu daman ganawa da shi ba.

KU KARANTA: Labari da dumi duminsa: Ojo Maduekwe ya Rasu

Amma mun samu daga majiya da dama cewa yarinyar ta mutu daga baya, sai mutane suka je farautar wadanda suka yi fyaden, suka kama guda 1 ,suka masa kunan gashin masara zagaye da masu kallo har hafsoshin yan sanda.

 

 

The post An kona wani mutum kurmus a Jihar Delta appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Nigerian newspapers 24/7.















Музыкальные новости






















СМИ24.net — правдивые новости, непрерывно 24/7 на русском языке с ежеминутным обновлением *