Buhari ya yabama sojojin Najeriya
-Shugaba Muhammadu Buhari ya jaddadama sojojin Najeriya goyon baya tare da godiyar gwamnatinsa a kan aikin da suke mai hadari .
-Shugaban kasar ya bukaci hukumomin tsaro da su Kara kaimi a kan yaki da suke da ta’addanci da tsageranci.
Shugaban kasa Muhammadu Buhari da shugaban hafsin sojin Najeriya mai suna Laftanat Janar Tukur Buratai
Shugaba Muhammadu Buhari ya jaddada goyon bayanshi ga hukumomin tsaro a kan yaki da suke da kalubalancin tsaro irin su Boko Haram da tsageranci Shugaban yayi bayanin ta bakin ministan tsaro Mansur Muhammad Dan Ali yayin da yake bukin bude wani gini na sojojin kasa a Abuja. Ya kuma yabama sojojin a kan yakin da suke da Boko Haram, ya umurce su da kara azama a kan hare-haren da suke kaimasu, yana mai cewa maganar tsaro ita ce mafi mahimmanci ga gwamnatinsa.
Jawabin yana cewa “Ina mai tabbatar maku cewa daya daga cikin abubuwan da suke da muhimmanci ga gwamnati na shine karfafa ma dakarun mu yadda zasu gudanar da ayyukansu. Zamu ci gaba da ba dakarun mu duk goyon bayan da zai basu karfin gwuiwar tafiyar da ayyukansu.
KU KARANTA : Abubuwa 10 da ya kamata ka sani game da Marigayi Cif Ojo Maduekwe
Ina mai yaba ma shuwagabannin dakarun mu a kan sadaukar da kai da kwazo da suke nunawa a kan shawo kan matsalolin tsaro da kasar ke fuskanta. Ina kuma yabama nasarar da ake samu a kan yaki da akeyi da ta’addanci a sashen arewa maso gabas”
The post Buhari ya yabama sojojin Najeriya appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Nigerian newspapers 24/7.
